SiyasaAfirka
MDD ta ce al'ummar DRC sama da miliyan 28 na bukatar abinci
March 27, 2025Talla
A wata sanarwar hadin gwiwa da Hukumar Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (WFP), da takwararta ta Bunkasa Noma da Samar da Abinci wato (FAO) sun bayyana cewa rikici tsakanin 'yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Ruwanda da dakarun gwamnatin Kwango ya sake maida hannun agogo baya a kokarin shigar da abinci da sauran kayan agajin jinkai yankin.
Karin bayani:Kwango ta zargi MDD da sakaci wajen daukar mataki kan M23
Babban jami'in Hukumar Abinci ta Duniya da ke kula da shiyyar Eric Perdison ya ce iyalai da dama na cikin garari, duba da cewa mutanen da ke fadi tashin noma domin su ciyar da iyalansu, su ne ke neman tallafin abinci a wannan lokaci.