SiyasaYemen
Bahar Maliya: Mai ya sa 'yan Huthi ke kai hari?
July 9, 2025Talla
Harin dai na zaman na biyu da suka kai a Tekun na Bahar Maliya cikin sa'o'i 24, kuma har kawo yanzu ma'aikatan ceto na kokarin lalubo sauran ma'aikatan jirgin ruwan da suka yi batan dabo bayan harin da 'yan Huthin suka kai masa ya haddasa nutsewarsa. Masu aikin ceto sun bayyana cewa babban jirgin ruwan dakon kayan kirar Eternity C da ke dauke da tutar kasar Laberiya, ya lalace sosai sakamakon harin da 'yan Huthin suka kai masa da ke zaman harinsu na farko a kan jirgin ruwan dakon kaya a wannan shekara.