SiyasaKenya
Kenya: Zargin neman kifar da gwamnatin Ruto
July 9, 2025Talla
A baya-bayan nan dai Kenya na fama da jerin zanga-zanga, wacce ta samo asali daga boren da matasan kasar suka yi a kan matsin tattalin arziki da cin-hanci da kuma cin-zarafin da jami'an 'yan sanda ke yi. Matasan dai sun yi boren ne tun a watan Yunin bara, biyo bayan yunkurin gwamnati na yin sababbin dokoki da tsare-tsaren haraji da ya janyo fushin al'ummar kasar. A wancan lokaci jami'an tsaro sun yi amfani da karfin tuwo wajen murkushe boren, abin da ya janyo asarar rayuka da ya sanya a bana ma matasan suka fito domin tuni da wadanda aka halaka a zanga-zangar ta bara.